Governor Inuwa Yahaya Hosts Tsangaya Teachers to Iftar

Image
 8th March, 2025  Governor Inuwa Yahaya Hosts Tsangaya Teachers to Iftar …As Forum Crowns Gombe Governor ‘Khadimul Qur’an’ …Lauds Him for Construction of Tsangaya Schools, Free Enrollment of Almajiri into Go-Health Governor Muhammadu Inuwa Yahaya, CON, has hosted the leadership of the Association of Tsangaya teachers from across the state to a special Iftar at the Government House, Gombe.  This was a continuation of the Governor’s tradition of hosting public Iftar for the citizens of the state, an occasion that provides Governor Inuwa Yahaya with another opportunity to deepen his engagement with the Muslim community and promote peace and brotherhood among all. Addressing his guests shortly after the iftar, Governor Inuwa Yahaya reaffirmed his administration’s commitment to improving the welfare of Tsangaya teachers and Almajiri children, acknowledging the significance of Qur’anic education in the society. The Governor stated that his government has ensured the provision o...

Gwamnan Gombe Ya Taya Aiyedatiwa Da sauran yan APC Murnar Nasarar Lashe Kujerar Gwamnan Ondo

 17/11/2024

Gwamnan Gombe Ya Taya Aiyedatiwa Da APC Murnar Nasarar Lashe Kujerar Gwamnan Ondo


Gwamnan Jihar Gombe Muhammadu Inuwa Yahaya CON, ya taya takwaransa na Jihar Ondo, Lucky Aiyedatiwa na Jam'iyyar APC murnar samun gagarumin rinjaye a zaɓen gwamnan Jihar Ondo da aka kammala, wanda ya ƙara tabbatar da aniyarsa ta jan ragamar jihar a wani sabon wa'adi.


Gwamna Inuwa Yahaya ya bayyana nasarar da Aiyedatiwa ya samu a matsayin nasarar da ta tabbatar da aminci da amanar da al’ummar Ondo suke da shi a ga jagorancinsa.


Yace babbar tazarar data baiwa gwamnan nasara ta nuna ƙarara irin goyon bayan tsarin tafiyar da mulki na Jam’iyyar APC da kuma shugabancinta na ƙasa ƙarƙashin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, wanda ke ci gaba da jan hankalin al’ummar Nijeriya.


A yayin da ya bukace shi da ya ci gaba da bin ka’idojin jam’iyyar na samar da ayyuka da shugabanci na gari, Gwamna Inuwa Yahaya ya kuma buƙaci gwamnan da aka sake zaɓa ya ci gaba da baiwa al’ummar Ondo fifiko da kuma ci gaba da gudanar da ayyukan raya ƙasa da za su yi kyakkyawan tasiri a rayuwarsu.


Ya kuma yi addu’ar Allah ya ci gaba da yi wa Aiyedatiwa da gwamnatinsa jagora, ya ba shi hikimar ci gaba da ayyukan alherin da ya fara.

Daga:

Ismaila Uba Misilli

Babban Daraktan Yaɗa Labarun Gwamnan Jihar Gombe

dailygombe.blogspot.com

Comments

Popular posts from this blog

Gombe SSG Prof Njodi celebrates Yazu's recognition by GSU

Ag. VC na Jami'ar Jihar Gombe GSU, ya jinjina wa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya bisa ba da fifiko ga ilimi.

AWARD: Njodi, Kallamu, Adamu,Umar Bags National leadership Award of Excellence.